Bakonmu a Yau
'Yan Najeriya na bukatar binciken musabbabin mutuwar Babban hafsan soji
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:37
'Yan Najeriya daga bangarori daban daban sun bukaci gwamnati da ta kafa kwamiti mai zaman kan sa da zai gudanar da bincike kan abinda ya yi sanadiyar hadarin jirgin saman sojin da ya kashe Babban hafsan sojin kasar Laftanar Janar Ibrahim Attahiru da 'Yan tawagar sa a ranar juma’a. Wannan shine karo na 4 da jiragen sojin saman Najeriya ke hadari a watannin baya-bayan nan. Dangane da wadannan kiraye kiraye, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya, kuma ga tsokacin da yayi akai.