Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Matsayin kungiyar Dattawan Arewacin Najeriya kan haramta kiwo a kudancin kasar

Wallafawa ranar:

Kungiyar Dattawan Arewacin Nigeria ta ce ba ta adawa da duk wani kyakkyawan tsari da gwamnati za ta bijiro dashi don kyautata sha‘anin kiwo da makiyaya Fulani ke yi domin tafiya daidai da zamani.

Wasu shanu mallakin makiyaya a  wani yanki na jihar Kaduna dake arewacin Najeriya.
Wasu shanu mallakin makiyaya a wani yanki na jihar Kaduna dake arewacin Najeriya. STEFAN HEUNIS/AFP/Getty Images
Talla

Sai dai kungiyar ba ta goyon bayan muzgunawa Fulanin makiyaya da sunan haramta musu kiwo.

A kwanakin baya ne dai Gwamnonin jihohin kudancin Nigeria 17 suka gabatar da bukatar hana kiwo a jihohinsu, bayan wani taro da suka yi a garin Asaba na jihar Delta.

Kan wannan batu Garba Aliyu Zaria ya tattauna da Dakta Hakeem Baba-Ahmed kakakin kungiyar Dattawan na Arewa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.