Yayinda lokacin zabe shugaban kasa zagaye na biyu ke ci gaba da karatowa, kungiyoyi daban a Jamhuriyar Niger na ci gaba da gudanarda taruruka hadi da addu'oi domin wayarda kan al'umma muimmancin zaman lafiya, salama da kwanciyar hankali wadanda su ne ginshikin bayan ci gaba da habaka tattalin arzikin kasa a cikin yanayin democradiya mai dorewa. Da wannan gurin ne hadin guiwar Ekkliziyoyin bishara na kungiyar Kristoci AMEEN ta shirya wani taro da gurin kare al'umma, tamkar riga kafi ga duk wani tashin hankali kafin lokacin da bayan zabe zagaye na biy da zai ja akalar Niger sake komawa ga tafarkn democradiya bayan juyin mulkin 18 ga watn Fabrairun 2010.