An kama mutane takwas bisa zargin su da kisan wasu ‘yan sanda a Jihar Deltan Najeriya
Wasu matane 8 sun shiga ragayar 'yansandan Najeriya a jihar Adelta akan aikakata laifin kisan wasu 'yan sandan kasar da ke bakin aikinsu.
Wallafawa ranar:
Jami’an tsaro a Najeriya sun cafke mutane takwas bisa zargin su da kashe ‘yan sanda takwas a garin Ughelli dake jihar Delta, kamar yadda kakakin Rundunar ACP Olumuyiwa Adejobi ya bayyana.
Ya kara da cewa a yayin wani bincike ne aka yiwa ‘yan sandan kwantan bauna inda aka kasha shida daga ciki sauran kuma suka tsere.
Adejobi ya ce Rundunar ta yi nasarar cafke mutane biyar da ake zargi da aikata laifin jim-kadan da aukuwar lamarin, yayin da sauran mutane ukun sai da aka tsaurara bincike aka yi kamo su a wurare mabanbanta.
Ya kara tabbatar da cewa Rundunar na aiki tukuru ba dare ba rana don ganin ta cafke tare da hukunta wadanda ke da hannu wurin aikata wannan laifi dama makamancinsa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu