Isa ga babban shafi

Najeriya ta tura sojoji domin ceto dalibai sama da 250 da aka sace a Kuriga

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu a yau Juma'a ya aike da sojoji domin ceto dalibai sama da 250 da wasu 'yan bindiga suka yi awon gaba a makarantar Kuriga da ke jihar Kaduna.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu. REUTERS - Afolabi Sotunde
Talla

Rahotanni na bayyana cewa harin na jihar Kaduna dai shi ne karo na biyu da aka yi garkuwa da jama’a a cikin mako guda a jihar da ta fi kowacce yawan jama’a a nahiyar Afirka, inda wasu gungun ‘yan fashi da makami a kan babura ke kai wa wadanda lamarin ya shafa hari a kauyuka da makarantu da kuma kan manyan tituna domin farautar kudin fansa.

Karin 'yan matan sakandaren Chibok guda biyu da sojojin Najeriya suka gano bayan tserewa daga hannun mayakan Boko Haram.
Karin 'yan matan sakandaren Chibok guda biyu da sojojin Najeriya suka gano bayan tserewa daga hannun mayakan Boko Haram. © RFI Hausa / Bilyaminu Yusuf

Ma’aikatan kananan hukumomin jihar Kaduna sun tabbatar da harin da aka kai na garkuwa da mutane a makarantar Kuriga a ranar Alhamis, sai dai ba su bayar da alkaluma ba domin a cewarsu har yanzu suna kan tantance yara nawa aka sace.

An harbe akalla mutum guda a yayin harin, kamar yadda mazauna yankin suka tabbatar.

Wani mazaunin garin Muhammad Adam shi ma ya shaida cewa an yi garkuwa da fiye da 280.

Wasu daga yan Boko Haram da aka mikawa kasar Chadi
Wasu daga yan Boko Haram da aka mikawa kasar Chadi © MNJTF

Sace jama’a da aka yi a Kaduna da kuma garkuwa da jama’a mako guda da ya gabata daga sansanin mutanen da mayakan jihadi suka raba da muhallansu a arewa maso gabashin Borno, ya kwatanta kalubalen da Tinubu ke fuskanta wanda ya yi alkawarin samar da tsaro a Najeriya.

Makamin roka makale jikin wata mota da mayakan Boko Haram ke amfani da shi a garin Damasak dake jihar Barno, an dauki hoton ranar 18 ga watan Maris shekarar 2015
Makamin roka makale jikin wata mota da mayakan Boko Haram ke amfani da shi a garin Damasak dake jihar Barno, an dauki hoton ranar 18 ga watan Maris shekarar 2015 ASSOCIATED PRESS - Jerome Delay

Satar jama'a guda biyu kuma ya zo ne kusan shekaru goma bayan mayakan Boko Haram sun sace dalibai a makarantar Chibok.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.