Isa ga babban shafi

Najeriya ta ce gargadin Amurka kan 'yan kasarta zai iya haifar da firgici

Gwamnatin Najeriya ta yi Allah wadai da shawar da Amurka ta baiwa ‘yan kasarta da ke a Najeriyan, tana mai cewar irin wadannan shawarar na iya haifar da firgici mara amfani da kuma yin illa ga tattalin arzikinta.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu. REUTERS - Afolabi Sotunde
Talla

A ranar 3 ga wannan watan ne dai, Amurka ta gargadi ‘yan kasarta da ke Najeriya kan barazanar da ake fuskanta a wasu daga cikin otel-otel da kuma biranen kasar.

Toh sai dai a yayin wata zantawa da manema labarai da ministan yada labarai da wayar da kan al’ummar kasar Mohammed Idris ya jagoranta a Abuja, ya ce irin wadannan shawarwari za su maida hannun agogo baya a kokarin da gwamnatinsu ke yi wajen gayyato masu zuba jari cikin kasar.

Ministan yada labaran Najeriya Mohammed-Idris.
Ministan yada labaran Najeriya Mohammed-Idris. © Daily Trust

Ya ce ako yaushe gwamnati na maida hankali wajen kare lafiyar al’umma da kuma bakin da ke ziyartar kasar.

“Mun samar da tsauraran matakan tsaro a matakin tarayya da na jihohi don tabbatar da tsaron masu yawon bude ido da kuma baki na kasashen waje. Wadannan matakan sun hada da tattara bayanan sirri da horas da jami’an tsaro da hadin gwiwa tare da hukumomin tsaron kasashen duniya da sauransu, don samar da tsaro."

Ministan ya kuma tabbatar da kokarin da jami’an tsaro ke yi wajen samar da tsaro a dukkanin fadin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.