'Yan Najeriya na bayyana maban-bantan ra'ayoyi kan tabbatar da nasarar Tinubu
'Yan Najeriya na bayyana ra'ayoyi maban-banta kan hukucin kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa da ta tabbatar da nasarar zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:30
Shugaban kotun, Mai shari'a Haruna Tsammani ya ce matakin hukumar zabe na ayyana Bola Tinubu, a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 25 ga watan Fabrairu shine dai-dai.
A zaman kotun na tsawon wuni guda a wannan Laraba dai an kori karar ɗan takarar shugaban kasa na babbar jam'iyyar adawar Najeriya, Atiku Abubakar da ma Peter Obi na jam'iyyar Labour da kuma jam'iyyar APM, wanda suka nemi kotun ta soke nasarar Bola Ahmed Tinubu a zaben Fabrairu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu