Isa ga babban shafi

Jihohi da garuruwan da za su fuskanci ambaliya a Najeriya

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Najeriya NEMA ta zayyana sunayen jihohi 14 da kuma garuruwa 31 da ta ce za su fuskanci ambaliyar ruwa sakamakon mamakon ruwan saman da za a tafka daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuki da muke ciki.

Ambaliyar ta mamaye garuruwa da dama a bara a Najeriya.
Ambaliyar ta mamaye garuruwa da dama a bara a Najeriya. REUTERS/Zohra Bensemra
Talla

Hukumar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da babban jami'in tsare-tsarenta reshen jihar Lagos, Mista Ibrahim Farinloye ya sanya wa hannu.

Farinloye ya bukaci masu ruwa da tsaki a wadannan jihohi da su dauki matakan hana samun asarar rayuka da dukiyoyi.

Jihohi da garuruwan da hukumar NEMA ta zayyana su ne kamar haka:

Filato: Langtang da Shendam

Kano: Sumaila da Tudun wada

Sokoto: Shagari da Goronyo da Silame

Delta: Okwe

Kaduna: Kachia

Akwa Ibom: Upenekang

Adamawa: Mubi da Demsa da Song da Mayo-belwa da Jimeta da Yola

Katsina: Katsina da Jibia da Kaita da Bindawa

Kebbi: Wara da Yelwa da Gwandu

Zamfara: Shinkafi da Gummi

Borno : Briyel

Jigawa: Gwaram

Kwara: Jebba

Niger: Mashegu da Kontagora

A bara  an samu ibtila'in ambaliyar ruwa da ya yi sanadiyar rushewar gidaje da lalata dukiyoyi har ma da samun salwantar rayuka baya ga harkokin kasuwanci da suka tsaya cak na wani dan lokaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.