Najeriya: An kashe Mutane 201 a Filato cikin watanni 5
Akalla mutane 201 ne aka bada rahoton sun mutu a cikin watanni biyar a hare hare 27 da aka kai kananan hukumomi 7 na jihar Filato da ke Najeriya, kamar yadda jaridar ‘Daily Trust’ da ake wallafawa a kasar ta ruwaito.
Wallafawa ranar:
Kashe kashen sun auku ne daga ranar 19 ga watan Janairu zuwa ranar 20 ga watan Yunin wannan shekarar da muke ciki.
Kanana hukumomin da wannan lamari ya shafa sune: Riyom, Bokkos, Jos ta Kudu, Jos ta Gabas, Barkin Ladi, Bassa da Mangu.
An tattara wadannan allkalumman ne daga kashe kashen da aka samu labarin su a jihar ne, kuma ana hasashen za a samu karuwar mamata.
Mazauna jihar da masu sharhi sun bayyana takaici a game da kashe kashen da ke aukuwa kwanan nan a jihar, inda suka ja hankali a kan makamancinsa a shekarar 2001, wanda aka kai shekaru sama da 10 ana yi, lamarin da ya lakume rayuka da kadarori da suka kai bilyoyin nairori.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu