Isa ga babban shafi

AFDB ya bukaci Tinubu ya rage kudin da ake kashe wa tafiyar da mulkin Najeriya

Shugaban Bankin Raya kasashen Afirka (AfDB), Dr. Akinwumi Adeshina, ya bukaci zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, da ya rage kudin da ake kashewa wajen gudanar da mulki.

Shugaban Bankin Raya Afirka Dr. Akinwumi Adeshina. Watan Nuwambar 2022
Shugaban Bankin Raya Afirka Dr. Akinwumi Adeshina. Watan Nuwambar 2022 © REUTERS/Emilie Madi
Talla

Adeshina wanda tsohon ministan Najeriya ne ya bayyana haka yayin taron bita da kwamitin mika mulki ta shirya gabanin rantsar da Bola Tinubu ranar Litinin a matsayin sabon shugaban kasar Najeriya.

Adesina ya ce makuden kudade da ake kashewa a bangaren gudanar da gwamnati ya ninka wanda ake kashewa wajen gudanar da ayyukan ci gaban kasa, kuma hakan na mummunan tasirin wajen hana ci gaban Najeriya a cewarsa.

Ba'a kashe kudin da ya kamata wajen raya kasa

Wani rahotan Majalisar Dinkin Duniya ya sanya Najeriya a matsayi na 167 cikin kasashe 174 da ke ware kudi da bai taka kara ya karya ba a fannin ayyukan ci gaba.

Ya roki Tinubu da ya tashi tsaye wajen kalubalantar mulki tun a ranar farko da zai karbi ragamar jagorancin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.