APC ta zabi shugabannin Majalisar Tarayyar Najeriya ta 10
Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta zabi Sanata Godswill Akpabio a matsayin wanda take son ya zama shugaban Majalisar Dattawan kasar ta 10, inda Barau Jibrin zai kasance mataimakinsa.
Wallafawa ranar:
Talla
Kazalika jam'iyyar ta APC ta sanar da Hon. Abbas Tajudeen matsayin kakakin Majalisar Wakilai, yayin da Ben Kalu zai zama mataimakinsa.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirye-shiryen rantsar da zababben shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a cikin watan Fabairu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu