Ruwa ya ci wasu mutane 5 a yayin da suke kokarin tsere wa 'yan bindiga a Abuja
Wasu mutane biyar da suka hada da maza hudu manya da matar aure daya sun nutse a ruwa, a lokacin da suke kokarin tserewa ‘yan bindigar da ke kokarin yin garkuwa da su, a kauyen Chakumi da ke unguwar Gurdi a karamar hukumar Abaji a birnin Abuja.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Bayanai sun ce mutanen da suka rasa rayukansu, suna tsaka da aiki a gona a lokacin da ‘yan bindiga suka yi kokarin kama su, da misalin karfe 11 na safiyar ranar Laraba.
Yayin wata zantawa da jaridar Daily Trust Najeriya, Sarkin Chakumi Muhd Magaji ya ce mutanen sun garzaya domin hawa kwalekwale su tsere zuwa kauyen Daku, amma a yayin da suke tsallaka kogin Gurara sai kwale-kwalen ya kife.
Basaraken ya koka da yadda ‘yaan bindiga suke cinkarensu babu babbaka ba tare da an kalubalance su baa, yana mai cewa yanzu al’ummarsa na tsoron zuwa gonakinsu.
Kakakin rundunar ‘yan sandan rundunar ‘yan sandan birnin tarayyar Abuja, adeh Josephine ba ta daga wayaa ba a lokacin da aka nemi karin bayani a game da lamarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu