Isa ga babban shafi

Duk wanda ya ce Najeriya kalau take yana bukatar gwajin kwakwalwa - Obasanjo

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya ce duk wanda ya ce Najeriya na cikin kwanciyar hankali akwai bukatar a duba shi, yana mai cewa bai kamata kasar ta kasance a inda take a halin yanzu ba.

Tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasenjo kenan
Tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasenjo kenan © Daily Post
Talla

Tsohon shugaban kasar ya bayyana haka ne a wajen taron lacca na shekara 15 na gidauniyar Wilson Badejo a birnin Legas.

“Najeriya ba inda ya kamata ta kasance a yau bane. Idan wani ya ce babu laifi a inda muke a halin yanzu, to kuwa akwai bukatar a duba kwakwalrsa,” a cewar sa.

Ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi zabin da ya dace a zabe mai zuwa domin a daidaita al’amura.

Ya kara da cewa, “Ko dai mu yi zabin da ya dace a 2023 domin idan muka yi zabin da ya dace za mu samu mafita.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.