Fasinjoji 16 sun bace sakamakon hatsarin jirgin ruwa a Legas
Kwanaki 3 kacal bayan hatsarin jirgin ruwa da ya yi sanadin mutuwar mutane 2 a yankin Ikorodu dake Lagos a Najeriya, wani karamin jirgin ruwan ya sake yin hatsari a yankin Mile 2 a daren Juma’a, inda yanzu haka ake neman fasinjoji 16 da ke cikinsa.
Wallafawa ranar:
Shugabar hukumar kula da sufurin ruwa a jihar Lagos, Sarat Braimah ce ta tabbatar da aukuwar lamarin a wata sanarwa a jiya Asabar.
Braimah ta ce har yanzu ba a gano inda ilahirin fasinjoji 16 da ke cikin jirgin ruwan suke ba.
Ta ce karamin jirgin ruwan da ya tashi daga Mile 2 zuwa Ibeshe a yankin Ojo ya karya daya daga cikin ka’idojin hukumar bayan da ya yi aiki cikin dare.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu