Alkalin Alkalan Najeriya Mai shari'a Ibrahim Tanko ya yi murabus
Rahotanni daga Najeriya sun ce alkalin alkalan kasar Mai shari’a Ibrahim Tanko ya mikawa shugaba Muhammadu Buhari wasikar murabus dinsa daga bakin aiki yau litinin.
Wallafawa ranar:
Cikin wasikar da Mai shari’a Ibrahim Tanko ya mikawa shugaba Buhari ya bayyana matsalar lafiya a matsayin babban dalilin da ya tilasta masa murabus.
Sai dai murabus din na mai shari’a Tanko na zuwa a dai dai lokacin da zarge-zargen rashawa ya dabaibaye shi bayan wata wasika da alkalan kotun koli 14 suka sanyawa hannu da ke nuna yadda alkalin alkalan ke tafka rashawa.
Tuni dai shugaba Muhammadu Buhari ya sanar da sunan Mai shari’a Olukayode Ariwoola a matsayin mukaddashin alkalin alkalan Najeriyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu