Isa ga babban shafi
Najeriya - siyasa

Biyayya ta ga Najeriya ce kawai, ba wani mahaluki ba - Osinbajo

Mataimakin Shugaban Najeriya Yemi Osinbajo yace biyayyar sa ga Najeriya ce kawai kamar yadda yayi rantsuwar kama aiki amma ba ga wani mahaluki ba kamar yadda wasu ke hasashe.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo. Premium Times
Talla

Yayin da yake jawabi wajen taron masu ruwa da tsaki a Jihar sa ta haihuwa, wato Jihar Ogun, wanda ya samu halartar Gwamna Dapo Abiodun da manyan Sarakunan Jihar, Osinbajo yace ba ya kai musu ziyarar yakin neman goyan baya bane, sai dai ya ziyarce su ne domin shaida musu aniyar sa ta tsayawa takarar shugabancin kasar.

Osinbajo yace rantsuwar aiki da yayi bayan nasarar zaben da suka yi, rantsuwa ce ga jama’ar Najeriya da yaran kasar da kuma makomar ta baki daya.

Mataimakin shigaban Najeriya, Prof. Yemi Osinbajo
Mataimakin shigaban Najeriya, Prof. Yemi Osinbajo © Prof. Yemi Osinbajo facebook

Mataimakin shugaban kasar yace ya tuntubi bangarori da dama dangane da aniyar sa ta tsayawa takara domin zama shugaban kasa, ciki harda shugaban Muhammadu Buhari kafin bayyana aniyar sa ga sauran ‘yan Najeriya.

Nayi kokari a shekaru 7 da na yi

Osinbajo yace a cikin shekaru 7 da yayi a matsayin mataimakin shugaban kasa ya bada gudumawa wajen aiwatar da sauye sauye a bangaren shari’a da kuma tabbatar da kare hakkokin alkalai.

Mataimakin shugaban kasar yace aiki da Buhari ya bashi damar fahimtar shugabanci a matakin koli da kuma sanya shi a matsayin wanda zai iya warware matsaloli masu girma kamar irin na tattalin arziki da tsaro da makamantan su.

Zan daura inda Buhari ya tsaya

Osinbajo yace yana da fahimtar aikin da zai iya dorawa daga inda wadanda suka gabace shi suka yi.

Goyon baya

Gwamna Abiodun ya bayyana cikakken goyan bayan sa ga takarar mataimakin shugaban kasar wajen zama shugaban kasa, inda yace yana da kwarewar da ake bukata wajen ci gaba da yiwa jama’ar Najeriya aiki.

Shima a nashi jawabi, Babban Basaraken Jihar, Alake of Egbaland, Oba Adeodotun Gbadebo ya tabbatar da kwarewar Osinbajo wajen tsayawa takarar, inda ya masa addu’ar sake dawowa fadar sa a matsayin shugaban Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.