Isa ga babban shafi
Najeriya-Taraba

Mutane 11 sun jikkata a harin bam din da aka sake kaiwa Taraba

Rundunar ‘yan sanda a Taraba, ta ce harin bam din da aka kai kan wata mashaya a jihar da ke arewa maso gabashin Najeriya ya yi sanadin jikkatar mutane 11, da suka hada da maza 10 da kuma mace 1.

Taswirar Taraba a Najeriya.
Taswirar Taraba a Najeriya. WorldStage
Talla

Bam din ya tashi ne a mashayar da ke unguwar Nukkai a wajen Jalingo, babban birnin jihar da misalin karfe 7 na daren ranar Juma'a da ta gabata, kamar yadda kakakin 'yan sanda Usman Abdullahi ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

Kakakin ‘yan sandan y ace bayanan da suka tattara sun nuna cewar, wani mutum da ba a gano wanene ba ne ya ajiye bam din cikin jakar leda a mashayar kafin daga bisani ya tarwatse.

A ranar Talatar da ta gabata ne dai, wani bam ya fashe a wata mashaya da ke garin Iware, inda mutane 6 suka mutu wasu 16 kuma suka jikkata.

Kwana guda bayan faruwar lamarin ne kuma kungiyar ISWAP ta dauki alhakin kai harin, abinda ke zama alamar farko ta bayyanar ta a jihar Taraba da ke arewa maso gabashin Najeriya, sabanin wuraren da ta saba kai hare-hare a yankin tafkin Chadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.