Isa ga babban shafi
Najeriya

Ma'aikatan jiragen kasa za su fara yajin aikin gargadi na kwanaki 3

Ma'aikatan sufurin jiragen kasa a Najeriya za su shiga yajin aikin gargadi na kwanaki 3 daga ranar Alhamis 18 ga watan Nuwamba zuwa 20 ga Nuwamba.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari lokacin da ya kaddamar  sufurin jirigen kasa na zamani da zai yi aiki tsakanin Lagos zuwa Ibadan.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari lokacin da ya kaddamar sufurin jirigen kasa na zamani da zai yi aiki tsakanin Lagos zuwa Ibadan. © Buhari Sallau
Talla

Babban sakataren kungiyar ma'aikatan layin dogo a Najeriya (NUR), Kwamared Segun Esan, ya tabbatar da haka, kuma rahotanni na cewa tuni kungiyar ta sanar da mahukunta Shirin shiga  yajin aikin.

A baya dai kungiyar masu aikin jiragen kasa ta Najeriya NUR da ‘yar uwarta, ta manyan ma’aikatan hukumar da kuma kamfanin na gwamnati, sun baiwa gwamnatin tarayya da hukumar kula da jiragen kasa ta kasa wa’adin makonni uku don biyan wasu bukatunsu da suka hada da karin albashi da alawus- alawus daga ranar 14 ga watan Nuwamba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.