Isa ga babban shafi

Shugaban Najeriya zai halarci taron yanayi na COP 26

Shugaban  Najeriya Muhammadu Buhari zai halarci taron sauyin yanayin da aka yiwa lakabi da COP26 a Glasgow dake Scotland, inda zai gabatar da irin matakan da kasar ke dauka wajen yaki da sauyin yanayi.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, yayin gaisawa da mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo, Gwamnan jihar Ekiti Kayode Fayemi da Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni. 20/8/2021.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, yayin gaisawa da mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo, Gwamnan jihar Ekiti Kayode Fayemi da Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni. 20/8/2021. © Buhari Sallau
Talla

Sanarwar da kakakin sa Garba Shehu ya rabawa manema labarai tace shugaban zai yiwa taron jawabi a ranar talata, yayin da kuma zai halarci wasu tarurruka da shugaban Amurka Joe Biden da shugaban Faransa Emmanuel Macron zasu jagoran ta.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari lokacin da ya tashi daga Abuja zuwa Glasgow da Paris
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari lokacin da ya tashi daga Abuja zuwa Glasgow da Paris © Nigeria presidency

Shehu ya kuma ce Buhari zai jagoranci taron ‘Yan kasuwa da masu zuba jari daga Najeriya da Faransa wanda zai gudana a birnin Paris inda ake saran halartar wakilan gwamnatocin kasashen biyu da yan kasuwa da jami’an diflomasiya da kuma Yan jaridu.

Sanarwar tace ziyarar Buhari Paris zata kuma bashi damar halartar taron zaman lafiya karo na 4 da shugaba Emmanuel Macron zai jagoran ta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.