Isa ga babban shafi
Najeriya

Malami ya maida martani kan bukatar biyan Igboho diyya

Gwamnatin Najeriya na shirin daukaka kara kan hukuncin wata babbar kotu a jihar Oyo da ke a birnin Ibadan, da ta umarci gwamnati da ministan shari’a su biya diyyar naira biliyan 20 ga mai rajin kare muradun kabilar Yarbawa Sunday Adeyemo, wanda aka fi sani da Igboho, a matsayin diyyar barnar da jami'an tsaron farin kaya na DSS suka yi masa yayin wani sumame da suka kai gidansa.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tare da Ministan shari'ar kasar Abubakar Malami
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari tare da Ministan shari'ar kasar Abubakar Malami The Whistler NG
Talla

Dan rajin dake naman ballewar yankin kudu maso yamamcin Najeriya na hannun hukumomin Benin a halin da ake ciki tun bayan tserewarsa lokacin da jami'an na DSS suka dira a gidansa.

To sai dai yayin da yake martani kan matakin cikin wata hira da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a Abuja Ministan Shari’a Abubakar Malami ya sanar da cewa za a daukaka kara kan hukuncin.

Tun bayan tserewar Sunday Igboho lauyoyinsa suka maka hukumar ta DSS da ministan shari'a na Najeriya a gaban kuliya, inda a madadinsa, suke neman a biya shi kudade saboda take hakkinsa na dan kasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.