'Yan bindiga sun tilasta wa mazauna wasu yankunan Sokoto gudun hijira
Mazauna karamar hukumar Sabon Birni a Jihar Sokoto na rayuwa ne a cikin bakin ciki sakamakon hare-hare, da barnar da ‘yan bindiga ke yi wa kauyen da kauyukan dake makwabtaka da su.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun nuna cewar, makwanni biyu da suka gabata ne ‘yan bingan suka dinga shiga kauyukan, tare da kashe akalla mutane dubu hamsin, da sace shanu.
Sakamakon wannan hare-haren dubban mata dake karamar hukumar Sabon Birni sun yi gudun hijira zuwa sakatariyar karamar hukumar, da makarantar firamari na Abdulhamid dake Sabon Birni.
Jaridar Daily Trust ta wallafa labarin dake cewa, da yawa daga cikin wadannan ‘yan Gudun hijiran sun koma Tudun Sunnah a jihar Maradi dake jamhuriyar Nijar, yayin da akwai wasu ‘yan gudun hijiran da yawa, da suka so tafiya kasar ta Nijar, amma baza su samu damar tafiya ba, sabo da wasu dalilai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu