Najeriya ta yi dacen samun Buhari a matsayin shugaba - Sarkin Daura
Sarkin Daura a jihar katsina Alhaji Umar Faruk Umar, ya ce Najeriya ta yi dacen samun Muhammadu Buhari a matsayin shugaba a daidai wannan lokaci da ta ke fuskantar kalubale.
Wallafawa ranar:
Ya ce ba don Buhari ne shugaban Najeriya ba a yanzu, al’amura za su rincabe sosai, yana mai cewa zai yi matukar wahala a samu damar taruwa a fadarsa.
Sarkin ya kara da cewa, al’ummar Daura sun ce moriyar kasancewar Buhari shugaban kasa, duba da yadda daidaikun mutane da kungiyoyi ke zuwa musu da ababen more rayuwa.
A nasa jawabin, Buhari ya bayyana farin cikinsa da kasancewa a mahaifarsa, inda ya yi tuni da yadda yake ziyartar fadar sarkin Daura a matsayinsa na shugaban mulkin soja a shekarun baya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu