Isa ga babban shafi

Kamfanonin sadarwar Najeriya sun fara aiwatar da dokar haramcin Twitter

Kamfanonin sadarwa a Najeriya da suka hada da MTN da Airtel da Glo da kuma 9Mobile sun fara toshe hanyar shiga shafin, Twitter a yau, kwana daya bayan da gwamnatin tarayya ta sanar da dakatar da shafin a Najeriya.

Logon kamfanin sadarwar sada zumunta na Twitter
Logon kamfanin sadarwar sada zumunta na Twitter © AFP
Talla

Kamfanonin sun ce sun samu umarni daga Hukumar Sadarwa ta Najeriya don toshe hanyoyin shiga shafin Twitter a kasar bayan dakatarwar na Gwamnatin Tarayya a ranar Juma’a.

'Yan Najeriyar masu amafani da shafin sun farka a ranar Asabar da fuskantar wahala wajen samun damar shiga shafukansu na Twitter yayin da wasu ke lalubo wasu hanyoyin sadarwar masu zaman kansu.

Fittatu sunyi tir da matakin

Tuni fitattun ‘Yan Najeriya da shahararrun suka fara nuna bacin ransu danagane da matakin na Gwamnatin Tarayya na hana amfani da Twitter a kasar, ba tare da la’akari da kutse da shisshigin da Twitter ke wa gwamnati ba.

Aisha Buhari ta rufe Twitter

Tuni mai dakin shugaban kasa Aisha Buhari ta rufe shafinta na Twitter, domin biyayye da umurnin da uban ‘ya’yan nata yayi.

"Zan rufe shafina na Twitter a yanzu. Fatan alheri ga Najeriya," kamar yadda ta rubuta gabanin rufe shafin.

PDP

Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta bi sahun wasu fitattu da suka hada mawaka da lauyoyi wajen Allah wadai da matakin gwamnatin tarayya na katse Twitter.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.