Buhari ya bukaci a kubutar da daliban Islamiyar da aka sace
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci hukumomin tsaro da na leken asirin kasar da su kara kaimi wajen maido da daliban makarantar Islamiya 200 da ‘yan bindiga suka sace a jihar Neja.
Wallafawa ranar:
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa, ‘yan bindigar da suka sace daliban makarantar Jangebe ta jihar Zamfara, su suka yi awon gaba da daliban Neja.
Shugaba Buhari ya yi Allah-wadai da wannan al’amari , yayin da ya umarci hukumiomin tsaro na gwamnati da su agaza wa iyalan yaran da aka sace.
A ranar Lahadi ne ‘yan bindigar dauke da muggan makamai kuma haye a kan babura suka dirar wa makarantar Islamiyar da ke garin Tegina na Neja , inda suka tattara dalibai da malamai suna tsaka da karatu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu