Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziya ga iyalan Babban hafsan sojan Najeriya
Uwar gidan shugaban Najeriya Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya ga iyalan Babban hafsan sojan Najeriya Janar Ibrahim Attahiru da ya rasu ranar Jumma’a sakamakon hadarin jirgin sama.
Wallafawa ranar:
Ta shafin ta na Twitta uwargidan shugban kasa, Aisha Buhari ta bayyana kai ziyarar ta’aziyar tare da wallafa hotunan ziyarar.
Aisha Buhari ta ziyarci iyalan Babban hafsan sojan Najeriya
I paid a condolence visit to the Family of the Late Chief of Army Staff, Lt. Gen. Ibrahim Attahiru.
— Aisha M. Buhari (@aishambuhari) May 23, 2021
The death of the Late Chief Of Army Staff and the other military officers aboard the ill-fated aircraft is a monumental loss to their families and the Nation at large. pic.twitter.com/8s1OB4Ntxj
A ranar Asabar aka binne Babban Hafsan sojan tare da sojoji 10 da suka mutu a hatsarin jirgin sama a Kaduna.
Aisha Buhari ta ce rasuwar babban hafsan sojin babban rashi ne ga iyalansa da kuma Najeriya baki ɗaya.
Rahin halartan shugaban kasa da mataimakin sa jana'iza
‘Yan Najeriya sun soki shugaban kasa da mataimakinsa kan rashin halartan jana’izan babban hafsan sojin Najeriyar da wasu mukarrabansa da akayi a Abuja.
Yayin da wasu sukayiwa Ministan tsaro Abubakar Malami da wasu gwamnonin jihohin kasar ca kan zabin halartan bukin aure maimakon karrama manyan sojojin da suka rasa rayukansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu