Isa ga babban shafi
Najeriya - Lagos

Al'amura sun tsaya cik a Oshodi dake Lagas bayan mamayar sojoji

Yanzu haka mazauna da fasinjoji na makale unguwar Oshodi dake birnin Legas, yayin da sojoji suka mamaye manyan wurare na unguwar.

Dakarun Najeriya a lokacin da suke shirin zuwa kasar Mali daga Kaduna a arewacin kasar.
Dakarun Najeriya a lokacin da suke shirin zuwa kasar Mali daga Kaduna a arewacin kasar. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Rahotanni sunce jami’an sojan sun mamaye unguwar ce,  da safiyar Alhamis don daukar fansar wani jami’in rundunar sojin saman Najeriya, wanda ake zargin wasu ’yan daba sun yi masa kisan gilla.

Al'amura sun tsaya

An lalata Motoci da dama, musamman na safa, yayin da wasu mutane suka fuskanci tsangwama daga fusatattun jami'an tsaro.

Wasu mazauna yankin da ke zuwa bakin aiki sun fada cikin rikicin yayin da dalibai suka tsere suka koma gida, kazalika 'Yan kasuwa sun tsare sun bar shagunsa, wasu kuma sun bar motocinsu kan titi.

Cunkuson ababen hawa

Lamarin ya kara tabarbarewar matsalar zirga-zirga a cikin wannan birni kasancewar yanzu babu wani motsi na shige da fitce daga bangaren na Oshodi inda sojojin suka mamaye.

Unguwar Oshodi ta haɗa wasu manyan sassan birnin Legas tana kuma dauke da babbar tashar motar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a shekarun baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.