Isa ga babban shafi
Wasanni

Matashin ɗan Najeriya ya zama lamba ɗaya a duniyar kwallon Tebur

Wani matashin dan Najeriya ya zama lamba daya a wasan kwallon teburi ajin maza na ‘yan kasa da shekaru 11 a duniya.

Matashin dan Najeriya Musa Mustapha da ya zama lamba daya a wasan kwallon teburi ajin maza na ‘yan kasa da shekaru 11 a duniya. 22 ga watan Afrelu 2021
Matashin dan Najeriya Musa Mustapha da ya zama lamba daya a wasan kwallon teburi ajin maza na ‘yan kasa da shekaru 11 a duniya. 22 ga watan Afrelu 2021 © Daily Trust
Talla

Matashin dan wasan Musa Mustapha wanda ke zaune a Abuja yana daga cikin ‘yan wasan kwallon tebur na Najeriya da suka lashe Gasar Wasannin Matasa ta ITTF a shekarar 2019 a kasar Ghana.

Shekaru uku kenan da suka gabata Hukumar kwallon tebur ta duniya ke bibiyar dan wasan, tun bayan da ya fara buga gasar cin kofin kwallon tebur ta Najeriya a birnin Lagos.

Kafin Mustapha wata 'yar masar ke rike da ajin mata

Mustapha ya zama ɗan Afirka na biyu da aka zaba a matsayin lambobi na ɗaya a duniya, baya ga Hana Goda ‘yar kasar Masar da itama ta kasance ta farko a ajin mata ‘yan kasa da shekaru 15 a shekarar 2020.

A cikin jerin ‘yan wasan da hukumar kwallon Tebur din da fitar Mustapha yazo na daya a duniya da maki 128, a ‘Yan kasa da shekaru 11, yayin da ya kasance na 17 a cikin rukunin ‘yan kasa da shekaru 13.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.