Buhari zai koma Ingila don duba lafiyarsa
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai yi balaguro zuwa Ingila domin duba lafiyarsa a gobe Talata kamar yadda fadarsa ta sanar.
Wallafawa ranar:
Mai magana da yawun fadar Buhari, Femi Adesina ya bayyana cewa, shugaban zai tafi birnin London na Ingila a ranar 30 ga watan Maris domin duba lafiyarsa kamar yadda ya saba.
Kafin tafiyar tasa, Buhari zai gana da hafsoshin tsaron Najeriya a sanyin safiyar Talatar, sannan ya dauki hanyar zuwa filin jiragen sama na kasa da kasa da ke birnin Abuja kamar yadda Adesina ya bayyana.
Fadar shugaban Najeriya ta tabbatar da shirye-shiryen Buhari na komawa Ingila don duba lafiyarsa
President Muhammadu Buhari proceeds to London, the United Kingdom, Tuesday March 30, 2021, for a routine medical check-up.
— Garba Shehu (@GarShehu) March 29, 2021
Ana sa ran Buhari zai koma Najeriya a cikin mako na biyu na watan Afrilun wannan shekara kamar yadda sanarwar fadarsa ta ce.
A shekarar 2017 ne, shugaban ya shafe tsawon kwanaki 100 a birnin London, inda ya yi wata doguwar jinyar cutar da har yanzu ba a bayyana ta ba, lamarin da ya haddasa cece-kuce a ciki da wajen Najeriya.
Wasu daga cikin ‘yan kasar musamman daga bangaren ‘yan adawa sun bukaci shugaban da ya sauka daga karagar mulki a wancan lokaci da ya dade yana jinya a London.
Shugaban ya dade bai yi tafiya zuwa kasar waje ba saboda annobar coronavirus wadda ta tilasta rufe kan iyakokin kasashen duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu