An sace shugaban karamar hukuma a Zamfara
An sace shugaban Karamar Hukumar Bakura da ke mazabar Gamji ta jihar Zamfara a Najeriya wato Sani Dangwaggo na Jam'iyyar APC mai mulkin kasar.
Wallafawa ranar:
Majiyar iyalansa ta ce, da misalin karfe 11 na daren da ya gabata wasu ‘yan bindiga suka yi awon gaba da shi daga gidansa da ke unguwar Gamji a daidai lokacin da ake shatata ruwan sama.
Sakataren Yada labaran Jam’iyyar APC a jihar Zamfara, Shehu Isa ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa, masu garkuwar sun tuntubi iyalansa, inda suka bukaci a biya su Naira miliyan 10 a matsayin kudin fansa.
Garkuwa da mutane don karbar kudin fansa ta zama ruwan dare a Najeriya, matsalar da har yanzu hukumomin kasar suka gaza magance ta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu