Abinda ya faru ga Zulum a Baga alama ce ta muma bamu tsira ba - Gwamnoni
Kungiyar Gwamnonin Najeriya ta ce farmakin da gungun maharan da ake kyautata zaton mayakan Boko Haram ne suka kaiwa tawagar gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum a garin Baga, alama ce dake nuna cewar su kansu gwamnoni basu tsira daga barazanar kungiyar ta Boko Haram ba.
Wallafawa ranar:
Shugaban kungiyar gwamnonin Najeriyar kuma gwamnan jihar Ekiti Kayode Fayemi ne ya fitar da sanarwar hadin gwiwar ga manema labarai, bayan taron da suka yi a ranar litinin a Abuja.
Taron gwamnonin da ya maida hankali kan sha’anin tsaro, ya koka kan yadda lamurra ke kara tabarbarewa a sassan Najeriya, duk da kokarin gwamnati na kawo karshen matsalar.
Ranar lahadin nan da ta gabata yayin karbar bakuncin gwamnonin Jigawa da Kebbi a Maiduguri, gwamna Babagana Zulum ya jadadda cewar, akwai wadanda ke yiwa gwamnati zagon kasa ga kokarinta na murkushe ta’addanci, matsalar da yace ba za ta bari a kawo karshen matsalar da yankin arewa maso gabshin kasar ke ciki ba.
A wani labarin kuma mai alaka da wannan, yau Talata 4, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gana da manyan hafsoshin tsaron kasar da sauran masu ruwa da tsaki a Abuja, taron da ake kyautata zaton ya tattauna ne kan irin koma bayan da ake samu ga kokarin kawo karshen matsalolin tsaro a Najeriyar, la’akari da abinda ya faru da gwamnan Borno a garin Baga.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu