Abin fashewa ya halaka mutane a Katsina
Fashewar wani abu da ake zaton bam ne a jihar Katsina dake Najeriya, yayi sanadin mutuwar mutane dakalla 5 tare da jikkata wasu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Majiyoyi da dama sun ce fashewar ta auku ne da safiyar yau Asabar, a wata gona dake kauyen ‘Yammama a karamar hukumar Malumfashi.
Kakakin ‘yan sandan jihar Katsina SP Gambo Isah yace kawo yanzu mutane 5 ‘ya’ya ga wani Alhaji Adamu aka tabbatar da mutuwarsu, koda yake wasu shaidun gani da iso sun ce mutane 6 suka mutu, yayinda wasu 6 suka jikkata.
Dukkanin wadanda suka rasa rayukan nasu dai yara ne, wadanda suka je gonar domin diban ciyawar dabbobi.
Katsina na daga cikin jihohin arewacin Najeriya masu fama da matsalar hare-haren ‘yan bindiga dake halaka rayukan jama’a, da kuma satar mutanen don karbar kudin fansa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu