Yawan masu cutar coronavirus a Najeriya ya zarta dubu 7
Cibiyar yaki da yaduwar cutuka a Najeriya NCDC, tace jumillar yawan wadanda suka kamu da cutar coronavirus a kasar ya kai dubu 7 da 16, bayan samun karin mutane 339 da suka kamu da cutar cikin sa’o’i 24 da suka gabata, tare da hasarar rayuka 9.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Cibiyar ta NCDC tace an samu sabbin mutanen da suka kamu da cutar ta coronavirus ce a jihohi 18, inda Legas kadai ke da mutane 139, sai Kano da Oyo masu mutane 28 kowannensu, yayinda Edo ke da 25, Katsina mutane 22.
A sauran jihohin kuma sabbin mutane 18 suka kamu da coronavirus a Kaduna, Jigawa da Yobe na da 14-14, sai Filato da Yobe masu 13-13, Abuja na da 11, Gombe 8, Ondo 5, sai kuma mutum guda-guda a Rivers da Adamawa.
Zuwa yanz jumillar mutane dubu 1 da 907 suka warke daga cikin dubu 7 da 16 da suka kamu da cutar ta coronavirus a Najeriya, yayinda 211 suka mutu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu