'Yan bindiga sun tilastawa mutane dubu 42 tserewa daga iyakokin Najeriya da Nijar - MDD
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla fararen hula dubu 42 ne suka tserewa hare-haren ‘yan bindiga daga kauyukan kan iyakar kasashen Najeriya da Nijar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Cikin bayanan da hukumar ta wallafa a shafinta, ta ce adadin kari ne kan wasu mutanen dubu 23 da karancin tsaro ya tilastawa tserewa daga yankunansu akan iyakar Najeriya cikin watan jiya, yayinda wasu karin fararen hula dubu 19 a Jamhuriyyar Nijar suka rasa matsugunansu wanda ke da nasaba da karancin tsaron da garuruwan kan iyaka ke fuskanta a kasashen biyu.
A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ce sakamakon tsoro da gujewa matsalar rashin tsaro a kan iyakokin kasar Nijar, ya tilastawa wasu al'ummar kasar dubu 19 zama yan gudun hijira a cikin kasarsu ta asali.
Hukumar ta ce jihohin Najeriya da a halin yanzu ke fama da rikice rikice sun hada da sokoto, da Katsina da Kuma Zamfara
Rahoton yace hari mafi muni a baya bayan nan shi ne na ranar 18 ga watan Afrilun da ya gabata inda akalla mutane 47 suka rasa rayuwarsu a jihar katsina
Yankin arewacin Najeriya dai yayi kaurin suna wajen fama da rikice-rikicen kabilanci musamman rikici a kan filaye da ruwa, sai kuma a baya bayan satar mutane da hare-haren ‘yan bindiga.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu