'Yan bindiga sun kashe mutane kusan 50 a Katsina
Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina da ke Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 47 a wani hari da ‘yan bindiga suka kaddamar kan wasu kauyuka da ke jihar.
Wallafawa ranar:
‘Yan bindigar sun hallaka jama’a a kauyukan da ke kananan hukumomin Danmus da Dutsinma da Safana, yayin da mutane da dama suka jikkata a harin na ranar Asabar.
Farmakin ya tilasta wa dimbin jama’a kaurace wa muhallansu.
Kodayake wasu rahotani sun ce, mazauna karkarar sun yi kukan-kura inda suka yi nasarar fatattakar ‘yan bindigar, yayin da suka yi ta kona karmami don nuna wa barayin cewa, lallai suna farke.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu