Isa ga babban shafi
Najeriya

Mun gano kwaryar tsafi cike da jini a Zamfara- 'Yan sanda

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara da ke Najeriya ta tabbatar da gano wata kwarya cike da jinin bil’adama daga wani mutun dan kungiyar asiri a garin Gusau.

An gano kwarya cike da jini, sannan kuma ga sunayen fitattun 'yan siyasar jihar Zamfara a wani gidan tsafi da ke jihar.
An gano kwarya cike da jini, sannan kuma ga sunayen fitattun 'yan siyasar jihar Zamfara a wani gidan tsafi da ke jihar. buzzgh
Talla

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sandan, Mohammed Shehu ya sanar da haka a yayin zantawa da manema labarai a yau Asabar.

A makon  jiya ne, rundunar ‘yan sandan ta kai samame gidan mutumin da ke wata unguwar masu hannu da shuni, bayan an kwarmata musu irin barnar da ake tafka wa a wannan gida.

A yayin wannan samame, jami’an ‘yan sandan sun gano kayayyakin tsafe-tsafe da suka hada da kwarya cike da jini da kuma wata takarda dauke da sunayen wasu fitattun ‘yan siyasa a jihar.

Yanzu haka ana ci gaba da gudanar da bincike kan al’amarin a cewar rundunar ‘yan sandan Zamfara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.