Bakonmu a Yau
Haj. Naja'atu Muhammed kan zargin da Rundunar Sojin Najeriya ta yi kan wasu mazauna Barno na baiwa Boko Haram bayanan sirri
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:20
Rundunar Sojin Najeriya ta zargi wasu mazauna Yankin Jihar Barno da bada bayanai kan sojojin kasar abinda ya yi sanadiyar kwantar baunan da mayakan Boko Haram suka musu, inda suka kashe kusan 50.Manjo Janar John Eneche, Daraktan yada larabai na ayyukan ma’aikatar tsaron Najeriya ya sanar da haka, inda yace sojojin na komawa ne daga alargano inda suka samu nasara, lokacin da wasu suka tseguntawa Boko Haram tafiyar su inda suka kai musu hari.Dangane da haka, Garba Aliyu Zaria ya tattauna da Hajiya Naja’atu Muhammed.