Najeriya
'Yan bindiga sun kai hari a Askira Uba
Wasu 'yan bindiga da ake kyautata zaton mayakan kungiyar boko haram ne sun kai hari kauyen Rumirgo dake Askira Uba a Jihar Barno inda suka kasha mutane 10 da kona gidaje da kuma satar abinci.
Wallafawa ranar:
Talla
Wani mazaunin Yankin Adamu Galadima ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewar sun kai harin ne da misalign karfe 5 da rabi na yammacin jiya, dauke da motar da aka dorawa bindiga mai sarrafa kan sa, inda suke harbi kan mai uwa da wabi.
Peter Malgwui dake zama a kauyen ya tabbatar da Yan bindigar sun kashe mutane 10 da kona gidaje da dama.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu