Sojin Najeriya sun halaka 'yan bindiga a Sokoto da Katsina
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana kame yan bindiga 25 da kuma halaka wasu da dama, yayin artabu da su a jihohin Katsina da Sokoto.
Wallafawa ranar:
Cikin sanarwar da ta fitar ta hannun Manjo Hakeem Otiki, rundunar sojin ta ce dakarun nata sun fafata ne da yan bindigar a yankunan Rabbah da Burkusuma a Sokoto, sai kuma Batsari, Safana da Kankara a jihar Katsina, sai dai babu karin bayani kan adadin yan bindigar da aka halaka.
Bayaga tarin makamai, sojin Najeriyar sun kuma yi nasarar kwace Babura akalla 25-daga hannun yan bindigar.
Ko a ranar Juma’ar da ta gabata, dakarun Najeriya sun yi nasarar halaka yan bindiga 15 a yankin Dansadau da ke jihar Zamfara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu