Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojin Najeriya sun halaka 'yan bindiga a Sokoto da Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana kame yan bindiga 25 da kuma halaka wasu da dama, yayin artabu da su a jihohin Katsina da Sokoto.

Wasu dakarun sojin Najeriya.
Wasu dakarun sojin Najeriya. Pulse.ng
Talla

Cikin sanarwar da ta fitar ta hannun Manjo Hakeem Otiki, rundunar sojin ta ce dakarun nata sun fafata ne da yan bindigar a yankunan Rabbah da Burkusuma a Sokoto, sai kuma Batsari, Safana da Kankara a jihar Katsina, sai dai babu karin bayani kan adadin yan bindigar da aka halaka.

Bayaga tarin makamai, sojin Najeriyar sun kuma yi nasarar kwace Babura akalla 25-daga hannun yan bindigar.

Ko a ranar Juma’ar da ta gabata, dakarun Najeriya sun yi nasarar halaka yan bindiga 15 a yankin Dansadau da ke jihar Zamfara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.