Isa ga babban shafi
Najeriya-Kano

An cafke kwamandan kungiyar IS a Kano

Hukumar jami’an tsaron farin kaya ta DSS, ta cafke wani kwamandan reshen kungiyar IS, reshen Afrika ta yamma, Haussieni Mai-Tangaran a garin Kano, da ta dade tana farautarsa.

Maykan Boko Haram suna gaisawa da 'yan uwansu fuesunoni da aka sako a amtsayin musayar 'yan matansakandaren Chibok.
Maykan Boko Haram suna gaisawa da 'yan uwansu fuesunoni da aka sako a amtsayin musayar 'yan matansakandaren Chibok. REUTERS/Zanah Mustapha
Talla

Hukumar ta ce Mai Tangaran ne ya shirya mafi akasarin muggan hare-haren da mayakan Boko Haram suka kai a sassan Najeriya, ciki harda mummunan harin a aka kai a garin Kano, na ranar 20 ga watan janairun shekara ta 2012.

Zalika hukumar ta DSS, ta ce Mai Tangaran ne ya shirya kai harin ta’addancin da ya hallaka daruruwan mutane, yayinda suke gabatar da Sallar Juma’a a masallacin gidan sarki a Kano, sai kuma harin da aka kaiwa barikin sojoji a jihar Yobe a shekarar 2015.

Kakakin hukmar ta DSS Tony Puiyo ya ce, sun kuma lalata shirin ‘yan ta’adda na kai muganna hare-hare a biranen Najeriya musamman a Lokacin bikin Sallah babba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.