Hare-haren kunar bakin wake sun haifar da fargaba a jami'ar Maiduguri
Hare haren kunar bakin wake da aka kai kwanan baya a jami’ar Maiduguri da ke Jihar Borno, ya kara haifar da fargaba da tsoro a tsakanin dalibai da kuma malaman Jami’ar ta fuskar sha’anin tsaro. Kimanin mutane 16 aka tabbatar da sun mutu a hare haren kunar bakin wake guda biyu da aka kai a Jami’ar ta Maiduguri a ranar Lahadi da dare da aka yi bikin Sallah. An sha kai hare hare a Jami’ar amma hakan bai sa an rufe makarantar ba, sai dai a kullum malamai da dalibai na cikin fargaba da daukar matakan kare-kai. Awwal Janyau ya taba kai ziyara Jihar Borno kuma ya diba matsalar tsaron a Jami’ar ta Maiduguri.
Wallafawa ranar:
Hare-haren kunar bakin wake sun haifar da fargaba a jami'ar Maiduguri
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu