Ba zan lamunci rarrabuwar kai a gwamnatin Najeriya ba - Buhari
Rahotanni sun ce shugaban Najeriya Muhd Buhari, yayi watsi da yunkurin wasu mukarraban gwamnatinsa, na ganin cewa ya sanya musu hannu kan wasu muhimman takardu ba ta hanyar tsallake mukaddashin shugaba, kuma mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Jaridar The Nation da ake wallafa ta a Najeriya, ta rawaito cewa, shugaba Buhari yaki bai wa mukarraban da suka tafi zuwa birnin London damar ganinsa, inda ya umarci da su mai dawa mukaddashin shugaban kasa farfesa Osinbajo muhimman takardun ya sa musu hannu a kai kamar yadda doka ta tanadar.
A cewar Buhari, ba zai lamunci duk wani yunkuri ba na haddasa rarrabuwar kai a gwamnatinsa.
Sai dai jaridar ta The Nation, ta rawaito cewar shugaba Buharin ya gana da mai dakinsa Aisha, a lokacin da ta kai masa ziyara a makon da ya gabata, ba kamar yadda wasu ke yadawa a shafukan dandalin sada zumunta be cewa, uwargidan shugaban kasar bata samu damar ganawa da maigidan nata ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu