Najeriya: An kame madugun kungiyoyin sata da garkuwa da mutane
Rundunar 'yan sandan Najeriya, ta samu nasarar kama wani kasurgumin mai sata da kuma garkuwa da mutane a birnin Legas, bayan shafe lokaci mai tsawo tana nemansa ruwa a jallo.
Wallafawa ranar:
Shugaban rundunar yan sandan ta musamman da aka fi sani da IRT, ACP Abba Kyari, ya shaidawa kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN cewa, mai laifin da ke amsa sunan Evans, wanda suka shafe tsawon lokaci suna nema ruwa a jallo, sun damke shi ne, a wani gidansa da ke Magodo a birnin Legas.
ACP Kyari, yace, mutumin ya kwashe akalla shekaru 7 yana shugabantar gungun masu sata da garkuwa da mutane daban daban, wadanda sukai nasarar amshewa mutane da dama biliyoyin nairori kafin sakin wadanda suka sace.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu