Isa ga babban shafi
Najeriya

Shugaba Buhari na Najeriya ya nanata burin kubutar da 'yan matan Chibok daga hannun Boko Haram

Yayin da ‘yan matar Chibok  ke cika shekaru uku hannun 'yan Boko Haram, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nanata burin Gwamnatinsa na ganin sun kwato sauran matan da aka sace daga hannun ‘yan kungiyar Boko Haram.

'Yan matan Chibok da aka sace a cikin wani hoto da kungiyar Boko Haram suka bayar bayan sun shafe shekara daya.
'Yan matan Chibok da aka sace a cikin wani hoto da kungiyar Boko Haram suka bayar bayan sun shafe shekara daya. AFP
Talla

Juma'a 14 ga watan Aprilu na shekara ta 2014 ne ‘yan matan na Chibok ke cika shekaru uku da  sace su daga makarantar Sakandare dake garin Chibok a Jihar Borno.

Gwamnatin Muhammadu Buhari ta karbo ‘yan mata fiye da 20 daga cikin ‘yan mata 270 da aka sace.

Shugaban Najeriya ya bayyana cewa Gwamnati na tattaunawa da ‘yan Boko Haram tare da taimakon wasu kungiyoyi daga ciki da wajen Najeriya domin ganin an sako ‘yan matan ba tare da an yi masu lahani ba.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.