Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya na bukatar taimako don share nakiyoyin da Boko Haram ta dasa

Babban Hafsan sojin Najeriya Laftanat Janar Tukur Buratai, ya bukaci taimakon kwarraru daga Majalisar Dinkin Duniya, wajen share nakiyoyin da mayakan Boko Haram suka dasa a yankunan da suka taba kwacewa, musamman dajin Sambisa.

Mayakan Boko Haram sun binne nakiyoyi a wuraren da suka karbe iko
Mayakan Boko Haram sun binne nakiyoyi a wuraren da suka karbe iko Reuters
Talla

Buratai ya bukaci taimakon ne yayin zantawa da manema labarai a garin Maiduguri, inda ya ce yawan nakiyoyin da mayakan suka binne yana kange sojoji isa zuwa wasu sassan dajin na Sambisa.

Masana harkokin tsaro dai sun ce da bukatar a gudanar da wannan aikin cikin gaggawa ganin hadurran dake tattare da barinsu na tsawon lokaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.