Isa ga babban shafi
Najeriya

Gurbataccen wake ya haifar fargaba a Najeriya

A Najeriya yanzu haka jama’a sun fara nuna fargaba dangane da bayyanar wani gurbataccen wake a cikin kasuwanni musamman a jihar Gombe da ke arewa maso gabashin kasar, waken da ga alama aka sanya wa maganin kashe kwari domin ajiye shi na dogon lokaci. To sai dai daga bisani an sake fito da irin wannan wake a cikin kasuwanni, lamarin da ya sa jami’an kiwon lafiya da sauran hukumomin da ke kula da ingancin kaya ke gargadin jama’a da su yi taka-tsantsan. Wakilinmu Shehu Saulawa ya gudanar da bincike dangane da haka ga kuma rahotonsa. 

Gurbataccen wake ya haifar da fargaba a kasuwanni musamman a jihar Gombe da ke yanki arewa maso gabashin Najeriya
Gurbataccen wake ya haifar da fargaba a kasuwanni musamman a jihar Gombe da ke yanki arewa maso gabashin Najeriya AFP / Lionel Healing
Talla

03:02

Gurbataccen wake ya haifar fargaba a Najeriya

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.