Isa ga babban shafi
Najeria-Kaduna

Jami'an tsaro sun janye daga kawanyar da suka yi wa Shi'a a Kaduna

Jami’an Soji da ‘Yan sanda a Najeriya sun janye daga kawanyar da suka yiwa mabiya Mazhabar Shi’a a Masallacin Markaz da ke titin Zango a Jihar Kaduna.

Mabiya Mazhabar Shi'a a Jihar Kaduna da ke Najeriya
Mabiya Mazhabar Shi'a a Jihar Kaduna da ke Najeriya
Talla

A jiya Talata ne dai jami’an tsaron suka yiwa mabiya Mazhabar Shi’a kawanya, yayin da suka taro domin gudanar da addu’o’i a Masallacin a ranar Ashura.

Wani shaidar gani da ido ya ce ba’a samu wani tashin hankali ba a wurin, kuma babu wanda aka kama, kasancewar kawo yanzu kowa ya watse daga wajen.

Tun da fari dai kimanin motocin jami’an tsaro 18 ne suka yiwa masallacin na Markaz kawanya kafin daga bisani wata kungiyar tabbatar da ‘yancin gudanar da ibada ta Addinin Musulunci da ke Birtaniya ta yi kira ga jami’an kan su janye.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.