Isa ga babban shafi
Najeriya

Buhari ya jinjina wa shugaban Facebook

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jinjina wa shugaban kamfanin sadarwa na facebook, Mark Zuckerberg game da kokarinsa na kara wayar da kan matasan kasar a fannin fasahar sadarwa.

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Yemi Osinbajo da kuma shugaban facebook, Mark Zuckerberg a birnin Abuja
Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Yemi Osinbajo da kuma shugaban facebook, Mark Zuckerberg a birnin Abuja naij.com
Talla

Shugaban ya yaba wa Zuckerberg ne bayan ya gana da shi a fadarsa da ke babban birnin Abuja a yau Jumma’a.

Saukin kan Zuckerberg wanda shi ne na biyar wajen arziki a duniya ya kayatar da  Buhari, musamman yadda matashin ya cakudu da talakawan Najeriya a ziyar da ya kai.

A cewar shugaba Buhari, ba su saba ganin fitattun mutane kamar Zuckerberg na sassarfa a kan tituna ba har ta gai ga yin zufa.

A na shi bangaren, Mr. Zuckerberg mai shekaru 32 ya yaba da irin fasahar da matasan Najeriya ke da ita musamman a bangaren sarrafa kwamfuta  kamar yadda ya gani a garin Yaba da ke jihar Legas a kudancin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.