Saraki ya mikawa Shugaba Buhari Sunanyen Ministocin da suka tantace
Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Abubakar Bukola Saraki ya mikawa shugaban kasar Muhammadu Buhari sunayen ministocin da Majalisar ta tantance a fadar sa.
Wallafawa ranar:
Saraki ya mika wa Shugaban takardar sunanyen ne tare da masu bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin majalisa wato Sanata Ita Enang da Abdurahman Kawu Sumaila.
Bayan kwarya-kwaryar bikin da aka yi a fadar, Saraki ya ce majalisar ta amince da duk kan mutane 36 da shugaban kasar ya aike mata domin nada su a matsayin ministoci.
A ranar 29 ga watan Oktoba, majalisar dattawan ta kammala tantance ministoci 36 da shugaba Buhari ya aika mata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu