Najeriya
Boko Haram: 'Yan Sanda sun kama matasa 121 a Lagos
Jami’an 'Yan sandan Jihar Lagos da ke tarayyar Najeriya sun cafke wasu matsa kimamin 121 da suka fito daga birnin Kebbi na Arewacin kasar sakamakon zargin cewa suna da alaka da mayakan Kungiyar Boko Haram.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
To sai dai daya daga cikin ‘yan uwan matasan Abdullahi Umar Kawoje ya shaida wa RFI hausa cewa matasan ba su da alaka da Boko Haram kuma suna da sana’ar hannun da su ke yi a birnin Legas.
Kawoje ya kara da cewa an kama matasan ba tare da wani makami a jikinsu ba kuma akasarin su ba su kai shekarun balaga ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu