Nigeria
Nijeriya ta shiga sawun kasashen da ke musguna wa 'yan jarida
KUNGIYAR Da ke kula da aikin jarida a Duniya, ta jefa sunayen Najeriya da Brazil a cikin sahun kasashe 10, da ake muzgunawa ‘Yan jarida kuma ba tare da hukunta wadanda aka kama da aikata laifin ba.Yanzu haka rahoton kungiyar yace akwai ‘Yan jaridu kusan 100 da aka kashe, kuma babu wani alamun daukar mataki daga gwamnatocin kasashen da aka kashe ‘Yan jaridun.Kasashen da ke sahun gaba sun hada da Iraqi da Somalia da Philliphines da Afghanistan da kuma kasar Rasha.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: